Majalisar Dattawa za ta hanzarta amincewa da kudurin kafa Dokar Tsaron Daji — Sanata Barau

Majalisar Dattawan Najeriya ta kuduri aniyar fifita amincewa da Dokar Hukumar Tsaron Daji ta Najeriya (NFSS) ba tare da bata lokaci ba.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ne ya bayyana hakan a karshen mako yayin da Kwamanda Janar na NFSS, Dr. Wole Joshua Osatimehin, ya jagoranci wata tawagar manyan jami’an hukumar a wata ziyarar girmamawa zuwa gidansa da ke Abuja.

Sanata Jibrin ya jaddada gaggawar bukatar kafa NFSS domin yaki da ’yan bindiga, ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifuka da ake aikatawa a dazukan kasar nan. Ya yaba wa Dr. Osatimehin da tawagarsa kan kokarinsu wajen inganta tsaro a kasa, yana mai cewa amincewa da dokar NFSS zai ba su damar aiki yadda ya kamata tare da sojoji, ’yan sanda, ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro, Hukumar DSS da sauran hukumomin tsaro.

“Mun yaba da kokarin ku da na jami’an ku wajen yaki da ’yan bindiga, garkuwa da mutane da sauran laifuka makamantansu. Gudunmawar da kuke bayarwa na da matukar amfani ga kasa. Idan aka amince da dokar NFSS, za ku samu karin damar yin aiki fiye da yanzu. A wasu kasashe akwai irin wadannan hukumomi da ke aiki a karkashin sunaye daban-daban kamar agro-rangers, forest guards ko forest security services. Abu mafi muhimmanci shi ne samun cikakkiyar hukumar da ke da isassun kayan aiki da kudade domin kare dazukanmu daga zama mafakar masu laifi,” in ji Sanata Jibrin.

Ya tabbatar wa da tawagar NFSS da goyon bayan cikakken na Majalisar Dattawa, yana mai alkawarin hanzarta aiwatar da dokar. “Za mu tsaya tsayin daka tare da ku domin ganin an amince da wannan kudiri cikin gaggawa. Kafin mu tafi hutu, wannan kudiri zai samu dukkan kulawar da ya kamata saboda yana cikin muradun kasa baki daya,” ya tabbatar.

A baya, Dr. Wole Joshua Osatimehin ya bayyana cewa ziyarar tasu na neman shawarwari da kuma sabunta bayanai ne ga Sanata Jibrin dangane da ci gaban da aka samu da kuma muhimmancin kammala dokar NFSS. Ya bayyana rawar da NFSS ke takawa wajen tattara bayanan sirri, musayar bayanai da kama masu laifi, wanda ya taimaka matuka wajen kara tsaron kasa.

Dr. Osatimehin ya bayyana cewa NFSS ta riga ta kafa ofisoshi na umarni da kulawa a dukkan jihohi 36 da babban birnin tarayya, inda aka tura dubban jami’an hukumar zuwa sassan kasar. Ya ce amincewa da dokar zai kara karfafa gwiwar jami’an da suka samu horo sosai tare da sauran hukumomin tsaro.

Mataimakin Kwamanda Janar na NFSS mai kula da leken asiri, Ambasada John Metchie, ya gode wa Sanata Jibrin saboda jajircewarsa wajen ganin an kammala aikin kudirin NFSS.

Ya yabawa jagorancin Sanata Jibrin da hadin gwiwarsa da Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wajen tallafa wa shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Sabuwar Fata.

Metchie, wanda kuma shi ne Daraktan Afrika na Kungiyar International Association of World Peace Advocates (IAWPA), ya bayyana goyon bayan da kudirin NFSS ke samu daga Majalisar Dattawa da Majalisar Wakilai. Ya nuna kwarin gwiwar cewa tare da jajircewar Sanata Jibrin, za a kammala aiwatar da kudirin cikin lokaci mai kusa.

Ya kara yabawa Dr. Osatimehin saboda jagorancinsa, sannan ya bukaci Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro da sauran masu ruwa da tsaki su hada kai domin ganin Shugaba Tinubu ya rattaba hannu kan dokar. Metchie ya jaddada cewa amincewa da kudirin zai kara karfafa tsaro a kasar, musamman a yankunan dazuka da wuraren da ba su da cikakken ikon gwamnati.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *